Breaking

Sunday, July 15, 2018

LAMARIN DUNIYA Page 01

🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺


♥πŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•Š *LAMARIN DUNIYA*♥ πŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•Š _(Labarin Zulaihat da Sadiq)_



*_NA:_*

*ALIYU MIKO MUH'D* πŸ‘¨πŸ½‍πŸ’»

*08184427958*

*mikoaliyu3@gmail.com*

*Wattpad:* *MIKOALIYU*
*_______________________*
*THE KING OF WRITER'S* πŸ‘‘



*© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUMπŸ„*
           ☆We the best ☆


Email:realhausafulaniwriters@gmail.com

Facebook:www.Facebook.com/REALHAUSAFULANIWRITTERSFORUM.com

follow us on facebook


https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R

*Insta garam*

https://www.instagram.com/p/BkZOMcIlfcw/?utm_source=ig_share_sheet&igshid=15q15b5oz4j2u&r=wa1

*Nasiha:*

πŸ•ŠπŸ’” *_ABUN DUNIYA MAI KAREWA NE YA KU Ζ³AN UWA MUSULMAI ZAN SO KU GANE HAKAN  IDAN HAR KUN FAHIMCE NI KAIDA KEDAI KAWAI KI KASANCE KIN/KA BAUTAWA ALLAH KA DOMIN KA SAMU RABAUTA DUNIYA DA KUMA LAHIRA...._* πŸ’”πŸ•Š

*GARGADI:*

```Ba'a yarda wani, ko wata su sarrafa wannan Rubutun ba ta ko wacce siga ba tare da amincewar mai shi ba ko kungiya don haka a kula a kiaye```


*_Har ila yau kungiyar mu mai al-barka ban manta da ku ba a wannan tafiya Allah ya bar zimunci_*

_RAHAMAT MUH'D RUFA'I NALELE:_
*_Allah Kara basira ya kuma bad a sa'a πŸ‘πŸ½_*


*INAIWA AL-UMMAR MUSULMI BAKI DAYA BARKA DA SALLAH.*

_Allah ya mai maita mana_




_Page-_ 0⃣1⃣



πŸ‡Έauri take tsulawa mai matukar ban al-ajabi surutu da mitar da take ya nuna alamar cewar tabbas ranta a bace yake, saboda tsabar saurin da take zabgawa na wuce misali yasa bata wani jima tana tafiya ba ta isa izuwa kofar wani babban gidan kasa wanda da ganin alamu gidan manyan mutane ne wanda suka jima a kauyen babu sallama bare kara ta make kofar gidan ta shige ciki cikin fusata.
      Karar buge kofar gidan da tayi ne yasa gabaki  Ι—aya ilahiran mutanen gidan suka firgegita kowa ya fito waje ganin abinda suka fito suka gani a waje ya sasu fisata ainun gabaki Ι—aya suka ja tsaki ko wa ya saita izuwa komawa Ι—akin sa babu wani abu da ta iya cewa in banda kutuntumo ashar,  mai karfi sannan ta biyo bayan ashar Ι—in dacewar: Shegu 'yan iska malalatan banza da na wofi wai ace tsabar wulakanci daga fitata unguwa sai kawai a karbi kuΙ—in girki na al-halin dukkan ku kunsan dacewar yau ranar girki na ce.
 
      Allah da girma yake yo inbanda abun ta  tunda har taga cewar tayi surutan da masifar babu wanda ya mata kallon kirki ballantana ya dubeta mai makon ta tsagaita sai ta cigaba da kutuntuma musu ashariya.
Haka dai tai tayi har ta gaji ta koma Ι—aki ganin surutun Inna Asabe ya lafa hakan ne yasa wata Tsaleliyar Budurwa  ma'abociyar kyawun fasali gami da tsarin halitta ta fito daga cikin wani Ζ™aramin daki wanda daganin a'lamu da ada can ba Ι—aki bane.

   Cikin sanΙ—a da tafiya tamkar wata barauniya ta Ι—auko, bokitin caples da wani katon tulu,  Ι—aukar tulun keda wuya sai ta sa gudu ta fito daga cikin gidan duk da tasan cewar ranar kashin ta ya bushe.

 Tun lokacin da ta fito daga gidansu Bata tsa gaita da fyalla gudun nan ba har sai da ta tabbatar da cewar ta iso bayan gari.

Ni da nake binta a baya ban iya komai ba face kallo da muka shiga cikin ruΙ—ani gami kauyanci domin komai iya gayun mutum,  idan ya kalli yanayin gurin zai yi matukar mamaki domim kuwa tabbas wajen ya amsa sunansa abin kallo.

    Cikin hanzari da Ι—aga Ζ™afa ta iso izuwa bakin wata Ζ™orama wacce ko da ace  ba'a damu Ι—ibar ruwan cikin ta to lallai ba Ζ™aramin so mutum zai yi ya ganshi ya kasance a tare da itaba wani sanyi take busawa marar cutarwa wanda idan zaka shekara a bakin wannan fadama kai da mura ko zafi sai wani ikon Allah.

     Wani Ι—an Ζ™aramin kwano ta Ι—auko acikin bokitin caples Ι—in ta samo kwaso ruwan a hankali domin bata shiga cikin sa saboda kiyaye lafiyar jikinta,  cikin nutsuwa da kamala ta kammala cika bokin ta kaf baki Ι—aya sannan ta koma kan tulun ruwanta shima ta cika.

   Kammalawar hakan ke da wuya a gareta sai tayi hanzarin Ι—aukar bokintin a ka sannan ta Ι—auki tulun a hannun ta tanufi izuwa hanyar komawa gidansu domin bata san mai zai faru da ita ba ayau.

   Tayi nisa cikin tafiyarta sai taga mutum tsulum a gabanta cikin firgici ta Ι—ago kai ta dube shi tana mai faΙ—in cewa subhanallahi.

    Haba yaya Sa'idu don Allah yanzu wannan wasa ne?  Gaskiya bana son irin wannan wallahi idan ka Ζ™aramin sai nai maka kuka.

Murmushi yayi sannan yace yi haΖ™uri Ζ™anwata na tuba, amma daga ina kike haka da yamma?  Wallahi Inna Asabe ce ta ake ni tun da safe na Ι—ebo mata ruwa a rafin bayan garin don tace min   tafi son ruwan can domin yafi tsafta da Ι—aΙ—in sha,  na Ι—auko tulu zan tafi sai Iya tace sai na kammala ayyu kan gida ban kammala aikin ba ni kuma sai wajen La'asar don gudun fushin Inna Asabe shiyasa ka ga na tahon yanzu idan ba haka ba duka zatamin wallahi.

   Hawaye ne ke zubowa daga fuskar Sa'idu yana mai cewa kiyi hakuri ZULAIHAT komai mai wucewa ne wata rana sai labari bani ruwan naki na kai miki gida ko don kiyi saurin zuwa kada taimaki faΙ—a hakan kuwa akai babu garda ta miΖ™a masa  ya karΙ“a ya Ι—ora a kansa sannan ya riΖ™e tulun ruwan a hannu, suka soma tafiya a cikin tafiyar tasu Sa'idu ya fuskaci Zualaiha babu annuri ko kwanciyar hankali a tattare da ita hakan ne ya bashi Ζ™arfin gwiwar Ι—auke mata tunanin ta da abubuwan dariya wani lokacin ma sai ya cakuleta da tsokana ita kuwa tai ta keta dariya kamar baza ta daina ba.



To Yan zu muka soma mai karatu sai ka Ι—aura Ι—amarar wanzuwa tare da niπŸ‘¨πŸ½‍πŸ’»


Nakune:


Mrs: *Ali*

No comments:

Post a Comment

Post Top Ad

Your Ad Spot

Pages